Pape Seydou N'Diaye

Pape Seydou N'Diaye (an haife shi ranar 11 ga watan Fabrairun 1993) ƙwararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne kuma ɗan ƙasar Senegal wanda a halin yanzu yake taka leda a matsayin mai tsaron gida a kulob ɗin Danish 2nd Division Jammerbugt FC.

Pape Seydou N'Diaye
Rayuwa
HaihuwaDakar, 11 ga Faburairu, 1993 (31 shekaru)
ƙasaSenegal
Karatu
HarsunaFaransanci
Sana'a
Sana'aɗan wasan ƙwallon ƙafa
Hanya
ƘungiyoyiShekaruWasanni da ya/ta bugaƘwallaye
  Senegal national association football team (en) Fassara-
 
Muƙami ko ƙwarewaMai tsaran raga

Sana'a

Kulob

Tun 2012 N'Diaye ya taka leda a ASC Niarry Tally.

A ranar 3 ga watan Nuwamban 2021, N'Diaye ya shiga kulob ɗin Danish 1st Division Jammerbugt FC kan yarjejeniya har zuwa cikin watan Yunin 2023. [1]

Ƙasashen Duniya

Bayan zaɓen da aka yi masa na gasar Olympics, N'Diaye ya halarci gasar cin kofin nahiyar Afirka na ƴan ƙasa da shekaru 23 na 2015 a ƙasarsa ta haihuwa. Senegal ce ta zo ta huɗu a gasar bayan ta sha kashi a hannun Najeriya a wasan kusa da na ƙarshe da kuma wasan ƙarshe a matsayi na uku a hannun Afirka ta Kudu .

N'Diaye ya buga wasansa na farko a babbar tawagar Senegal a ranar 10 ga watan Fabrairun 2016, a wasan sada zumunci da suka doke Mexico da ci 2-0 a Miami. [2] Ya halarci gasar cin kofin nahiyar Afirka ta 2017 da aka yi a Gabon.

Manazarta

Hanyoyin haɗi na waje

  • Pape Seydou N'Diaye at WorldFootball.net
  • Pape Seydou N'Diaye at FootballDatabase.eu