Emil Sambou

Emil Sambou (an haife shi a ranar 11 ga watan Mayun, 1994) ƙwararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne ɗan ƙasar Gambia wanda ke buga wasan gaba a ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Afirka ta Kudu Engen Santos FC da kuma ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Gambia.

Emil Sambou
Rayuwa
Haihuwa11 Mayu 1994 (30 shekaru)
ƙasaGambiya
Sana'a
Sana'aɗan wasan ƙwallon ƙafa
Hanya
ƘungiyoyiShekaruWasanni da ya/ta bugaƘwallaye
Santos F.C. (en) Fassara-
 
Muƙami ko ƙwarewaAtaka

Sambou ya koma Santos bayan nasarar jarrabawar gwaji da ƙwarewar fasaha a lokacin rani na shekarar 2016.[1] Bayan ya shiga kungiyar, dan wasan ya yi hasashen cewa zai zura kwallaye 15 a kakar wasa ta farko a kungiyar. [2]

Ya zura kwallaye biyu a ragar Cape Town All Stars a wasan da suka tashi 3-3. [3]

Ayyukan kasa da kasa

An kira Sambou zuwa tawagar kwallon kafar Gambia domin buga wasan zagaye da Senegal.[4]

Ya zura kwallaye biyu a wasan sada zumunci da Gambia a wasan da suka doke Gambiya Ports Authority FC 3-2.[5]

Manazarta

Hanyoyin haɗi na waje

  • Emil Sambou at National-Football-Teams.com
  • Emil Sambou at Soccerway